Skip to main content

Gwamnan Kano ya jinjinawa Uba Maga Yakasai kan bunkasa shirin ciyar da dalibai

 


 


Gwamnan Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya jinjinawa shugaban shirin ciyar da daliban makarantun Firamare da Sakandare a jihar Kano Alhaji Uba Maga Yakasai, bisa irin kokarin da yake yi wajen bunkasa ciyarwar, ta hanyar fito da sabbin tsare-tsaren kawo ci gaba a harkar.

Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya yi jinjinar ne, lokacin da ya kai ziyarar bazata Makarantar First Lady dake Mariri Hotoro.

Gwamna Abba Kabir, ya yabawa Alhaji Uba Maga kan yadda yake aiki cikin gaskiya da rikon amana tare da jajircewa.

Ya kara da cewa, a dai-dai jihar Kano tana bukatar irinsu Uba Maga don su tallafa mata wajen gyara barnar da gwamnatin baya tayi, yana mai cewa Alhaji Uba Maga ne kadai zai iya gyara barnar da aka yi bangaren ciyar da dalibai, tare da fito da sabbin hanyoyin da za a kara inganta harkar.

A cewar gwamna Abba Kabir. salo da tsarin shugabancin Alhaji Uba Maga ya banbanta dana sauran, shiyasa tun daga lokacin da aka nada shi ake ta samun ci gaba a fannin ciyar da dalibai.

A nasa jawabin shugaban shirin ciyar da dalibai na jihar Kano Alhaji Uba Maga Yakasai ya godewa Gwamna Abba Kabir Yusuf kan nada shi wannan babban mukami.

Ya kara da cewa a lokacin da ya karbi aiki, ya tarar gwamnatin baya ta lalata harkar gaba daya, har ta kai ga an dena ciyar da dalibai a makarantu da dama, saboda irin badakaloli da aka samu.

A cewar Alhaji Uba Maga Yakasai abun da ya fara yi shi ne, tsaftace tsarin tare da cusawa ma’aikata dabi’ar yin aiki cikin gaskiya da rikon amana.

Wanda hakan ya taimaka kwarai da gaske wajen kawo gagarumin sauyi cikin kankanin lokaci.

A karshe, Alhaji Uba Maga Yakasai ya bukaci gwamnan Kano Injiya Abba Kabir Yusuf ya ci gaba da tallafa masa do samun gudanar da aikinsa yadda ya kamata.

 

 

Comments

Popular posts from this blog

Youthful Excellence Personified: The Inspiring Story of Dahir M Hashim

  By Sule Sani Sule In a world where youthful exuberance is often marred by self-interest and fleeting passions, it's refreshing to come across individuals like Dahir M Hashim, the Commissioner for Environment and Climate Change in Kano State. His remarkable story serves as a beacon of hope, reminding us that the youth of today can indeed drive positive change. Hashim's journey is a testament to the power of dedication, hard work, and a genuine commitment to creating a better world. Long before he assumed his current role, he was already making significant contributions to the field of climate change and environmental affairs. His expertise and passion have not gone unnoticed, as evidenced by his appointment as Commissioner by Governor Abba Kabir Yusuf ¹. Under Hashim's leadership, the Ministry of Environment and Climate Change has undergone a remarkable transformation. His efforts have been instrumental in tackling environmental challenges, and his commitment to sustainabi...

Aisha Garba’s Bold Vision for Transforming Basic Education in Nigeria

By Suhaib Auwal   In a country where the foundational pillars of education have long been riddled with structural gaps, funding constraints, and policy inconsistencies, the recent leadership at the Universal Basic Education Commission (UBEC) signals a renewed hope.  Since her appointment as the Executive Secretary of UBEC, Aisha Garba has embarked on a reformist mission that seeks not just to address the surface-level symptoms, but to cure the systemic ailments crippling Nigeria’s basic education sector. At the core of her vision is a comprehensive, inclusive, and technology-driven approach to strengthening basic education delivery. Her leadership style is not only proactive, but it also reflects a deep understanding of Nigeria's complex educational terrain.  With over 17 million children currently out of school, Garba has made it unequivocally clear: this figure is unacceptable, and she intends to drastically reduce it within the shortest possible time. A Three-Pronged V...

DISRESPECTING COURT ORDER REGARDING KANO EMIRATE CRISIS

   By Dr. Usman Suleiman Sarki Law and order are the bedrock of harmonious living in every human society.  This necessitated the establishment of judicial system responsible for the enforcement of law and order as well as the settlement of disputes between parties.  One most important organ of the judiciary is the Court that determines cases brought before it using appropriate legal procedures. In an effort to ensure the proper discharge of its duties, the court gives order(s) to individuals, group, organizations/institutions and state mandating them to refrain or undertake an action before or after judgement. In line with the above, a federal high court sitting in Kano received a petition seeking for its intervention on matters relating Kano Emirate Crisis as the state House of Assembly passed a bill for the dissolution of the Five Emirates in the state where the court gives an order restraining the Kano state Governor from assenting a bill into and implementing the...