Adana Tarihi Da Al'ada: Shugaban Hukumar Tarihi Na Kano, Arc. Ahmad Zai Karbi Kyautar Kasa Kwanan Nan
Daga Salisu Maisaje
Manajan Daraktan Hukumar Tarihi Da Al'adu Ta Jihar Kano, Arc. Ahmad Abba Yusuf na sahun gaba kan sunayen da a ke bincike a kan su dan ba da lambar girmamawa kan hobbasa wajen raya al'adu da kuma alkinta tarihin al'umma.
Hadaddiyar kungiyar kungiyoyin dake nazari kan tarihi da al'adu na yammacin Afirka, dake da ofis a jihar Edo, ta shirya tsaf dan bayyana sakamakon wadanda su ka yi fice kan kudurorin da a ka yi nazari a kansu a shekarar da ta wuce ta 2025, na irin wadannan hukumomi.
Bayanan farko farko na nuni da cewa Manajan Daraktan na Kano ya na sahun gaba saboda la'akari da yadda yake kokari wajen ganin ya kara dawo da kima da muhimmancin hukumar cikin shekarar da ta gabata.
An gano cewar jihar Kano ta jima ba ta kula da muhimmancin hukumar a gwamnatocin baya. Amma daga zuwan gwamna Eng Abba Kabir Yusuf sai abubuwan su ka fara samun canji. Musamman yadda ya yi hangen nesan ba wa Arc. Ahmad shugabancin wajen.
A yadda labari ya same mu mun gano cewar, Arc Ahmad mutum ne wanda ke tafiyar da shugabancinsa bisa dattako duk da cewar ba yawan shekaru gare shi ba. Kuma ya kasance mai kishin cigaban jihar Kano ne tare da al'ummar ta.
Wannan yabon da zai samu, babban abu ne sa zai kara kusanta wasu hukumomin duniya da wasu gwamnatocin kasashen waje masu rajin fafutukar kara alkinta tarihi da al'adun mutanen dake doron wannan duniya ta mu.
Bayanan farko farko na wannan bincike da hadaddiyar kungiyar ta ke daf da kammalawa, sun nuni da cewar, a jihohin arewacin Najeriya, jihar Kano ce kadai ta ke cikin wadanda ke sahun gaba na cin wannan lambar yabo.
An kuma kara da cewa, shi shugaban hukumar tarihi da al'adun na jihar Kano, mutum ne wanda yake bin tsarin tafiyar da aikin gwamnati sau da kafa. Hakan ya kara tabbatar da gaskiyar sa da rikon amanar sa.
Maisaje ya rubuto wannan ne daga Abuja

Comments
Post a Comment